SAHEL ENTERTAINMENT: HAUSA

Follow us on Facebook

ads

Hot

Post Top Ad

Showing posts with label HAUSA. Show all posts
Showing posts with label HAUSA. Show all posts

Friday, March 15, 2019

'Rana mafi muni' a New Zealand

4:36 PM 0

A kalla mutum 49 ne aka kashe kuma sama da 20 suka samu raunuka masu muni bayan da aka kai hari a masallatai biyu a Christchurch da ke New Zealand. An kama mutum hudu da ake zargi suna da hannu a harin- an bayyana daya daga cikinsu dan kasar Ostireliya a matsayin mai tsattsauran ra'ayin ta'addanci. Shugabanni da mutanen duniya sun yi Allah-wadai da harin inda gwamnatin kasar ta sha alwashin hukunta maharan. Gwamnatin New Zealand ta shawarci musulmai da su kulle masallatansu har sai baba ta gani.

https://www.bbc.com/hausa/labarai-47587706

Read More

Sarkin Kano ya yi kira ga al'ummar Kano

11:30 AM 0

Sarkin Kano Muhammadu Sanusi na ll ya yi kira ga al'ummar Kano da su zauna
lafiya kuma su kwantar da hankali da kuma kiyaya yada jita jita.
Wannan kiran na zuwa ne bayan da aka gudanar da zaben gwamnoni da kuma 'yan
majalisar jiha a fadin kasar a ranar 9 ga watan Maris.
Sarkin ya bayyana cewa hukumar INEC ce kadai ke da 'yancin bayyana sahihin
sakamakon zabe, inda hukumar ta bayyana cewa zaben bai kammala ba, kuma
akwai wasu mazabu da za a sake zabe a jihar. Daga nan, sarkin ya yi godiya ga kwamishinan 'yan sandan jihar CP Mohammed Wakili da sauran jami'an tsaro musamman kan irin rawar da suka taka wajen kare rayuka da dukiyoyin al'ummar jihar.
Tun bayan da hukumar zaben kasar ta sanar da cewa zaben jihar bai kammala ba,
ake samun fargaba a jihar.
Jigga-jigan manyan jam'iyyun jihar Kano, Ganduje da Kwankwaso sun nemi
jama'ar jihar da su zauna lafiya.
Hakan na zuwa ne a ci gaba da zaman dar-dar da ake yi a cikin jihar lokacin ake
jiran sakamakon zaben a ranar Litinin.
A ranar Lahadi ne wasu magoya bayan wasu 'yan takara suka fara murnar lashe
zaben, wanda hakan ya sanya rundunar 'yan sandan jihar ta yi gargadi da a
daina, kuma a jira hukumjar zabe ta bayyana sakamako.
Babban jami'in tattara sakamako zabe a Kano Farfesa B.B Shehu ne ya sanar da
cewa ba a kammala zabe a Kano ba, a ranar Litinin.
Ya ce Abba Kabir Yusuf na babbar jam'iyyar hamayya PDP ya samu kuri'a 1,014,474
yayin da gwamna mai ci na jam'iyyar APC Abdullahi Umar Ganduje ya samu kuri'a
987,819.
Jam'iyyar PRP ce ta zo a matsayi na uku da kuri'a 104,009.
An ki bayyana wanda ya lashe zaben ne saboda bambancin kuri'un da ke tsakanin
manyan 'yan takarar ba shi da yawa.
Abin da ya sa dole a sake zabe a wasu mazabu da tun da farko aka soke su.
Hukumar INEC dai ba ta bayyana ranar da za ta sake gudanar da zabukan ba
tukuna.

Source: https://www.bbc.com/hausa/labarai-47542283

Read More

Friday, March 8, 2019

Batun Aurena Da Jamila Nagudu Farfaganda Ce Ta Siyasa, – Mai Mala Buni

12:28 AM 0
Dan takarar gwamnan jihar Yobe kuma sakataren jam’iyyar APC na kasa, Alhaji Mai Mala Buni ya karyata jita-jitar da ake ta yadawa a wasu kakafun sadarwa na bogi cewa zai auri fitacciyar jarumar finafinan Hausa, wato Jamila Nagudu.

Mai Mala Buni ya ce labarin ba shi da madogara bare tushe, kawai yarfe ne irin na masu adawar siyasa.
A yayin tattaunawarsa da jaridar RARIYA, sakataren na APC ya bayyana cewa hoton sa da aka dinga yadawa da jaruma Jamila Nagudu ba wai shi da ita kadai bane suka dauka, sun dauka ne da sauran abokan sana’arta a yayin ziyarar da suka kawo masa a matsayin sa na jigo a jam’iyyar APC. Amma sai aka yanke aka bar iya shi da ita don kawai biyan bukatar masu adawa.
“Kowa ya san yadda gwamnatinmu ta APC take da alaka da ‘yan fim din Hausa da na Turancin da kuma mawaka. Kuma sun bada gudummawa matuka a nasarar da APC ta yi a zaben 2015. Wanda hakan ya kara dankon zumunci tsakanin su da shugaba Buhari da sauran jiga-jigan APC”, cewar Mai Mala Buni.
Mala Buni ya kara da cewa yana daga cikin irin gudummawar da mawaka da ‘yan fim suka bayar a wannan gwamnati, irin wakoki da finafinan da suka yi a kan gwamnatin Buhari. Don haka akwai kyakkyawar alaka taakanin su da ‘yan fim a siyasance.
Sannan kuma irin ziyarar da ‘yan fim din suka kai masa sun kai shugaba Buhari irin ta a Villa ba sau daya ba sau biyu ba.
An zargi wani hadimin dan takarar gwamnan jihar Yobe a PDP, mai suna Najib da yada farfagandar auren, wanda kuma wannan ba shine karo na farko ba da yake yada farfaganda a kan jiga-jigan APC na jihar Yobe.
“Jam’iyyar APC ta jama’a ce musamman talakawa da matasa wanda hakan ya sa a koda yaushe matasa suke yawan ziyartar wasu jiga-jigan APC domin nuna goyon bayan su ga gwamnatin Buhari.
Read More

Shugaba Buhari ya isa Daura gabannin zaben gwamna shugaba-buhari-ya-isa-daura-gabannin-zaben-gwamna.html

12:18 AM 0
A yammacin ranar Alhamis, 7 ga watan Maris, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya isa garin Daura gabannin zaben gwamna da na majalisar jiha wanda za a gudanar a ranar Asabar, 9 ga watan Maris. 




Kamfanin dillancin labaran Najeriya (NAN) ta ruwaito cewa Shugaban kasar ya isa Daura a cikin jirgin Shugaban kasa mai saukar ungulu da misalin karfe 6:50 na yamma tare da rakiyar hadimansa da iyalansa makusantansa. Ya samu tarba daga sarkin Daura, Alhaji Farouk, mataimakansa da kuma daruruwan masoyansa. 

SOURCE: LegitHausa
Read More

Thursday, March 7, 2019

‘Yan bindiga sun kashe mutum 30 a Zamfara

2:58 PM 0


Daga jihar Zamfara ana cewa wasu ‘yan bindiga sun kaiwa kauyen Kware hari inda suka kashe mutane akalla mutum 30 a karamar hukumar Shinkafi.
An kai harin ne a tsakiyar daren ranar Lahadi, bayan kashe mutanen da ‘yan bindigar suka yi sun kone gidajen mutane da dama.
Rahotan bayyana cewa, an birne wadanda aka kashe a kauyen.


source: Http//:aminiya.dailytrust.com.ng
Read More

Ban mutu ba, Ina Lafiya Kalau – Masoyin Buhari da ya sha ruwar kwata

1:48 PM 0
Jita-jitan mutuwar Aliyu ya mamaye ko ta ina a yanar gizo duka, amma abin mamaki Aliyu Mohammed Sani ya fito ya bayyana da cewa bai mutu ba. kamar yadda gidan jaridan Daily Trust ke bada tabbacin haka.

“Alkawari ne nayi da cewa idan har shugaba Muhammadu Buhari ya lashe tseren takaran kujerar shugabancin kasar Najeriya a karo ta biyu ga zaben 2019, zan yi wanka da ruwar kwata, zan kuma sha kwata”
“Na kuma cika alkawari na. A yayin da aka gabatar da Buhari a matsayin mai nasara ga zaben, na shiga kwata kamar yadda na yi alkawari, na kuma sha ruwar kwatan a gaban jama’a. Duk wata zancen cewa na mutu sakamakon aman jini ko wata ciwon ciki, ba gaskiya bane. Ina lafiya lau, kuma ina garau” Inji Aliyu.
Sahel Entertainment ta gano cewa Aliyu na da aikin hannun sa na fenti.
“A yadda ni ke gabatar da wannan bayanin, ina shirye kan komawa Bauchi daga wata aikin fenti da ya kawo ni inda nake yanzun nan” inji shi.
Karanta Labarin:N-power 2019  
 
Read More

2019N-Power: Gwamnatin Tarayya sun bayyana lokacin da za a saki fom na N-POWER

1:30 PM 0
Gwamnatin tarayya ta samu labarin cewa mutane da dama ana rudan su da cewa  fom na N-Power ta shekarar 2019 ya fito. Harma wasu sun bayar da kudin su a layin yanar gizon ga mutanen da basu sani ba, wai don su taimaka masu da cika fom din. Bisa ga wannan dalilin ne ita gwamnatin tayi kira ga mutane da su lura sosai wajen yin mu'amala da 'yan damfara mussamman ta hanyar yanar gizo. da kuma gujewa duk wani labari da yazo musu game da N-power idan ba ta hanyar sadarwarsu ta Twitter, facebook da sauransu ba. Kana da haka gwamnatin ta kara da cewa fom din na daf da fitowa. saboda haka mutane su kara da hakuri

Sahel Entertainment tayiyi alkawarin sanar da ku  a duk lokacin da aka fara cikawa tare da matakai da zakabi domin cika fam din idan lokaci ya gabato. Mun bukaci ka bi wannan shafi na mu; Sahel Entertainment a kowace lokaci. A nan ne zamu sanar maku da cikakken labari da kuma matakan da za a dauka har ka kai ga cika fom din ba tare da samun wata matsala ba.

Mista Afolabi Imoukhuede, Babban shugaba mai taimakawa ga shugaba Muhammadu Buhari wajen samar da ayuka a kasa, ya bayyana a shafin yanar gizon nishadarwa ta Facebookr da cewa lallai gwamnatin tarayya bata bude layin cika fom na N-Power ba tukun na, amma za a yi hakan idan an kamala zaben tarayya ta Najeriya gaba daya.
“Gwamnatin tarayya bata saki fom na N-Power ba tukun na, amma za ta yi hakan bayan an kamala hidimar zaben kasar Najeriya gaba daya” inji fadin Mista Afolabi a layin Facebook da N-Power ke amfani da ita a ranar 20 ga watan Fabrairu, 2019 da ta gabata.
“Zamu kuma sanar da duk wata mataki akan hakan idan lokaci ya yi na sake cika fom din” inji shi.
Mista Afolabi ya gabatar da hakan ne a yayin da yake mayar da martani ga jita-jita da tambayoyi da mutane ke ta aikawa game da zancen fom na N-Power ta shekarar 2019.
Read More

Post Top Ad